Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta yi watsi da rahotannin sake dawo da rajistar masu kada kuri’a a wasu kananan hukumomin jihar Imo da cewa yaudara ce kawai.
Hukumar ta dakatar da aikin ci gaba da rijistar masu kada kuri’a (CVR) a kananan hukumomin Orsu, Njaba da Ihitte Uboma bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari wata cibiyar rijistar.
An kashe daya daga cikin ma’aikatan INEC, Anthony Nwokorie a harin yayin da aka yi awon gaba da wasu biyu.
A cewar sanarwar da kwamishinan INEC na kasa kuma shugaban kwamitin yada labarai da wayar da kan masu kada kuri’a, Festus Okoye, ya fitar, ya ce: “An jawo hankalinmu ga rahotannin kafafen yada labarai na cewa, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta dawo da ci gaba da rijistar masu kada kuri’a (CVR) a wuraren da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC. tun farko an dakatar da atisayen a jihar Imo. Wannan yaudara ce.