Hukumar zabe mai zaman kanta INEC, ta karbi kashin karshe na na’urorin tantance masu zabe gabanin babban zaben ƙasar da ke tafe.
A cikin wata sanarwa da Babban Kwamishina a Hukumar, Festus Okoye ya fitar, kwamishinan ya ce shugaban Hukumar Zaɓen ne farfesa Mahmood Yakubu tare da wasu manyan kwamishinoni a hukumar suka karɓi na’urorin a filin jirgin saman Nnamdi Azikwe da ke Abuja jiya Talata.
Hukumar zaɓen ta samar da filayen jirage hudu a Abuja da Kano da Legas da kuma Fatakwal a matsayin wuraren rarraba na’urorin cikin sauki zuwa sauran jihohi.
Har ila yau, sanarwar ta ce yanzu hukumar na’urorin tantance masu zaɓe da za a kai zuwa rumfunan zaɓe a fadin ƙasar .