Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya, Farfesa Mahmood Yakubu, ya gayyaci shugabannin jam’iyyu don yin zama kan rahotannin far wa juna da magoya bayansu suka yi a wasu jihohi.
Yakubu ya bayyana hakan ne a jiya Talata, yayin wani shiri na horar da jami’an zabe kan amfani da na’urorin zamani a zabukan 2023 da ke tafe a cikin kasar, inda kuma ta ce ‘yan sandan kasar za su kashe kudi naira biliyan 13 domin sayen makamai gabannin zabukan.
Jaridar Punch a Najeriya ta ruwaito cewa far wa juna da magoya bayan jam’iyun suka yi na zuwa ne makonni uku da soma yakin neman zabe da kuma sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da ‘yan takarar shugaban kasa suka yi karkashin jagorancin kwmaitin samar da zaman lafiya ta kasa.
Kafin soma yakin neman zabe a ranar 28 ga watan Satumba, an yi ta samun cacar baka tsakanin magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu da kuma na jam’iyyar Labour, Peter Obi.
Wani bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta wanda ya nuna mambobin wata kungiya na zagin dan takarar shugaban kasa na gaba-gaba ya janyo fushi da kuma Alla-wadai a fadin kasar.
Kafin faruwar lamuran, ‘yan sanda sun gargadi ‘yan siyasa da magoya bayansu kan yin kalaman kiyayya da kuma cin zarafi a intanet, inda ta yi barazanar hukunta wadanda aka samu da laifi.