fidelitybank

INEC ta gayyaci shugabannin APC da na PDP a kan farwa juna

Date:

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya, Farfesa Mahmood Yakubu, ya gayyaci shugabannin jam’iyyu don yin zama kan rahotannin far wa juna da magoya bayansu suka yi a wasu jihohi.

Yakubu ya bayyana hakan ne a jiya Talata, yayin wani shiri na horar da jami’an zabe kan amfani da na’urorin zamani a zabukan 2023 da ke tafe a cikin kasar, inda kuma ta ce ‘yan sandan kasar za su kashe kudi naira biliyan 13 domin sayen makamai gabannin zabukan.

Jaridar Punch a Najeriya ta ruwaito cewa far wa juna da magoya bayan jam’iyun suka yi na zuwa ne makonni uku da soma yakin neman zabe da kuma sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da ‘yan takarar shugaban kasa suka yi karkashin jagorancin kwmaitin samar da zaman lafiya ta kasa.

Kafin soma yakin neman zabe a ranar 28 ga watan Satumba, an yi ta samun cacar baka tsakanin magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu da kuma na jam’iyyar Labour, Peter Obi.

Wani bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta wanda ya nuna mambobin wata kungiya na zagin dan takarar shugaban kasa na gaba-gaba ya janyo fushi da kuma Alla-wadai a fadin kasar.

Kafin faruwar lamuran, ‘yan sanda sun gargadi ‘yan siyasa da magoya bayansu kan yin kalaman kiyayya da kuma cin zarafi a intanet, inda ta yi barazanar hukunta wadanda aka samu da laifi.

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp