Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ce, ta fara raba katinan zabe na dindindin guda 23,871 ga sabbin masu rajista a jihar Gombe.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Mohorret Bigun ya fitar ranar Alhamis a Gombe.
Bigun ya ce, PVCs 23,871 da aka karba na wadanda suka yi rajista ne ko kuma suka nemi sabunta bayanai, canja wuri ko maye gurbin katunan da suka bata ko lalace.
A cewar sa, an raba ne ga wadanda suka yi rajista a zangon farko da na biyu na shirin ci gaba da rijistar masu kada kuri’a (CVR) da ake gudanarwa tsakanin ranakun 28 ga watan Yuni zuwa 20 ga Disamba, 2021.
“Saboda haka, duk wadanda suka yi rajista ko suka nemi a maye gurbinsu da PVC a lokacin, ana karfafa su da su ziyarci ofisoshin INEC da ke fadin kananan hukumomin inda rumfunan zabe ke zaune don karbar PVC daga ranar Alhamis 21 ga Afrilu, 2022.”
Ya kuma ba da tabbacin wadanda suka yi rajista a rubu’in farko na shekarar 2022 da kuma wadanda ake gudanar da aikin a yanzu cewa za a yi amfani da na’urar tantance masu kada kuri’a kafin zaben 2023.
Bigun ya yi kira ga ‘yan Najeriya da suka cancanci shekaru 18 zuwa sama, da su yi rajista.