fidelitybank

INEC ta fara rabon katin zaɓe na shekarar 2023

Date:

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ce, ta fara raba katinan zabe na dindindin guda 23,871 ga sabbin masu rajista a jihar Gombe.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Mohorret Bigun ya fitar ranar Alhamis a Gombe.

Bigun ya ce, PVCs 23,871 da aka karba na wadanda suka yi rajista ne ko kuma suka nemi sabunta bayanai, canja wuri ko maye gurbin katunan da suka bata ko lalace.

A cewar sa, an raba ne ga wadanda suka yi rajista a zangon farko da na biyu na shirin ci gaba da rijistar masu kada kuri’a (CVR) da ake gudanarwa tsakanin ranakun 28 ga watan Yuni zuwa 20 ga Disamba, 2021.

“Saboda haka, duk wadanda suka yi rajista ko suka nemi a maye gurbinsu da PVC a lokacin, ana karfafa su da su ziyarci ofisoshin INEC da ke fadin kananan hukumomin inda rumfunan zabe ke zaune don karbar PVC daga ranar Alhamis 21 ga Afrilu, 2022.”

Ya kuma ba da tabbacin wadanda suka yi rajista a rubu’in farko na shekarar 2022 da kuma wadanda ake gudanar da aikin a yanzu cewa za a yi amfani da na’urar tantance masu kada kuri’a kafin zaben 2023.

Bigun ya yi kira ga ‘yan Najeriya da suka cancanci shekaru 18 zuwa sama, da su yi rajista.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...
X whatsapp