Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta dakatar da aikin rajistar masu kada kuri’a a karamar hukumar Igboeze ta Arewa da ke jihar Enugu, sakamakon harin da aka kai wa ma’aikatanta a yankin.
Wasu ‘yan bindiga sun kai hari kan jami’an hukumar da ke gudanar da rijistar zabe tare da kona ofishinta a yankin Igboeze ta Arewa.
Duk da cewa ba a samu asarar rai ba, akwatunan zabe 748, dakunan zabe 240, kayan ofis da kayan aiki sun lalace.
Hukumar ta bayyana hakan ne a ranar Alhamis a wata sanarwa da Festus Okoye, kwamishinan yada labarai da wayar da kan masu kada kuri’a ya fitar.
A cewar sanarwar da INEC ta fitar, Jude Okwuonu, sakataren gudanarwa a Enugu, ya ruwaito cewa, an kai harin ne da misalin karfe 2:30 na ranar Laraba a makarantar Community Primary School Umuopu da ke Umuozzi mazaɓa 19 a karamar hukumar Igboeze ta Arewa.