Hukumar Zaɓe inec, ta dakatar da dukkan ma’aikatan da aka samu da sakaci lokacin zaɓen shugaban ƙasa da ya gudana a ranar asabar da ta gabata 25 ga watan Fabirairu.
INEC ta ce dukkansu ba za su yi aikin zaɓen da za a yi ba na ‘yan majalisar jiha da na gwamnonin a ƙasar da za a yi a ranar 11 ga watan Maris.
Shugaban hukumar Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana hakan a wata tattaunawa da ya yi da kwamishinonin zaɓe a ranar Asabar a Abuja.
“Yayin da muke tunkarar zaɓen gwamna da na ‘yan majalisar jiha, dole mu ƙara ƙoƙari domin shawo kan matsalolin da muka fuskanta a zaɓen da ya gabata. ‘Yan Najeriya ba za su yarda da wani abu ba bayan wannan.
“Dukkan ma’aikacin da aka samu da sakaci, ma’aikacin INEC ne ko kuma na wucin gadi ne, cikin harda masu tattara sakamako da turawan zaɓe to ba za mu kyale su yi aikin zaɓen mai zuwa ba.
“Dole kwamishinonin zaɓe su ɗauki matakan da suka dace a wuraren da aka samu hujjojin cewa an yi abubuwa ba daidai ba,” in ji Farfesa Mahmood.