Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC, ta mikawa zababben shugaban kasa, Bola Tinubu da abokin takararsa Kashim Shettima takardar shaidar cin zabe.
Shugaban INEC na kasa, Yakubu Mahmood ya mika takardar shaidar cin zabe ga Tinubu da Shettima a Abuja ranar Talata.
Tinubu ya lashe zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar Asabar bayan ya kada kuri’u mafi rinjaye inda ya doke abokin takararsa na jam’iyyar Peoples Democratic Party, Atiku Abubakar, da Peter Obi na jam’iyyar Labour.