Hukumar zaɓe INEC, ta bai wa Alhassan Ado Doguwa shaidar sake cin zaɓe a matsayin ɗan majalisar wakilai daga mazaɓar Doguwa da Tudun Wada.
Karo na biyar kenan, da ɗan majalisar na tarayya ke samun nasarar zuwa majalisar wakilai daga Kano tun bayan dawowar Najeriya mulkin dimokraɗiyya a 1999.
Tun da farko dai an soke nasarar da ya samu, bayan zaɓen 25 ga watan Fabrairu, saboda jami’in sanar da sakamako, Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai ya ce “tursasa masa” aka yi.
Sai dai, jami’in sanar da sakamako a zaɓen cike-giɓi na mazaɓar, Farfesa Sani Ibrahim a ranar 15 ga watan Afrilu, ya ayyana Alhassan Doguwa a matsayin wanda ya yi nasara bayan wannan zaɓe.