Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta tabbatar da karuwar bukatar rajistar masu zabe.
Festus Okoye shugaban kwamitin yada labarai da wayar da kan masu kada kuri’a ya fitar da sanarwa a ranar Juma’a.
Jami’in ya ce, rahotannin da ake samu daga jihohin sun nuna cewa, an samu karuwar aikace-aikacen da ba a taba yin irinsa ba da kuma kalubalen da ‘yan kasar ke fuskanta.
Ya yi nuni da cewa, dukkan kwamishinonin zabe (RECs) sun yi taro a ranar Alhamis domin duba lamarin.
Okoye ya sanar da sakin karin injuna 209 zuwa Jihohin Kudu maso Gabas guda biyar da Legas da kuma Kano, inda matsalar ta fi kamari.
Alkalan zaben dai sun yi alkawarin sanya ido kan lamarin nan da ‘yan kwanaki masu zuwa tare da sake ganawa, domin duba yadda aikin ke gudana.
INEC ta kara da ba da tabbacin cewa, za a bi duk wani mataki na bai wa ‘yan Najeriya da suka cancanta damar cin gashin kansu. In ji Daily Post.
Sanarwar ta kara da cewa, “Kowane dan Najeriya da ya kai shekaru 18 zuwa sama yana da ‘yancin yin rajista da zabe a duk fadin kasar da yake zaune ba tare da wata tsangwama ba”.