fidelitybank

INEC na kokarin murde zaben Adamawa – Atiku

Date:

Tsohon shugaban mataimakin shugaban kasa wanda kuma ya yi wa jam’iyyar PDP takarar shugaban ƙasa a babban zaɓen da ya gabata, Atiku Abubakar, ya roƙi hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa, INEC a jihar Adamawa ta ayyana Jam’iyyarsa da ɗan takararta Ahmad Umar Fintiri a matsayin waɗanda suka yi nasara a zaɓen gwamnan jihar da aka yi ranar Asabar.

Atiku ya shaida wa BBC cewa bisa alƙaluman da aka wallafa a shafin INEC, PDP ce kan gaba da APC wadda Aishatu Dahiru Ahmed Binani ke yi wa takara.

Karanta Wannan: Umar Bago ya lashe zaben gwamnan Neja a APC

A cewarsa, an gudanar da zaɓe lafiya ba tare da wata matsala ba, inda ya yi zargin cewa ana ƙoƙarin yin murɗiya saboda jan ƙafar da ake yi wajen sanar da sakamakon zaɓen ƙaramar hukuma ɗaya da ake taƙaddama kan sakamakonta.

Tuni dai hukumar INEC ta sanar da sakamakon ƙananan hukumomi 20 na jihar.

Atiku Abubakar ya ce rashin sanar da sakamakon ƙaramar hukumar Fufore a kan lokaci na iya haifar da illa ga zaman lafiyar jihar Adamawa.

A halin da ake ciki dai manyan jam’iyyun da ke fafatawa a zaɓen na iƙirarin samun nasara a zaɓen

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp