fidelitybank

INEC na cigiyar dakataccen Kwamishinan da ya ayyana Binani a matsayin gwamnan Adamawa

Date:

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, a ranar Juma’a, ta bayyana cewa ba ta da masaniyar inda aka dakatad da kwamishinan zabe na reshen jihar Adamawa, Yunusa Hudu Ari.

A ranar Asabar din da ta gabata ne Ari ya haifar da cece-kuce a lokacin da ya ayyana Aisha Binani ta jam’iyyar APC a matsayin wadda ta lashe zaben cike gurbin kujerar gwamnan jihar Adamawa.

Ari dai ya ayyana Binani ne a matsayin wanda ya lashe zaben yayin da INEC ba ta kammala tattara sakamakon zaben ba.

Amma, INEC ta yi fatali da sanarwar Ari tare da sanar da Ahmadu Fintri a matsayin wanda ya lashe zaben bayan kidaya sakamakon.

Sai dai mai magana da yawun hukumar ta INEC, Festus Okoye, ya ce Ari bai amsa kiran nasa ba tun lokacin da ya dauki wannan aika-aika.

Da yake bayyana a gidan Talabijin na Channels, Okoye ya ce: “Ba mu san inda yake ba, domin bayan faruwar wannan lamari, hukumar ta rubuta masa takarda kuma ta kira shi a waya.

“Bai taba mayar da ko daya daga cikin kiran ba; bai amsa ko daya daga cikin kiran ba.

“Mun nemi ya kai rahoto ga Hukumar ranar Lahadi, ba mu gan shi ba, mun ce ya kawo rahoto ranar Litinin, ba mu gan shi ba. Don haka har zuwa yanzu, bai bayar da rahoto ba kuma ba mu san inda yake ba.”

punch newspaper headlines today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp