Hukumar zaɓe, INEC, ta fara rarraba kayan zaɓen gwamnoni da ƴan majalisun dokoki jihohi da za a yi ranar Asabar mai zuwa 18 ga watan Maris.
Tun a ranar Lahadi hukumar ta bayar da tabbacin cewa zuwa jiya Talata, za ta kammala aikin saita na’urorin tantance masu zaɓe na BVAS, waɗanda aka yi amfani da su a zaɓen shugaban ƙasa da ƴan majalisun dokoki na tarayya ranar 25 ga watan Fabarairu.
Na’urorin dai su ne za a yi amfani da su domin gudanar da zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisun dokokin jihohi da za a gudanar a ƙarshen mako.

Rahotanni sun ce zuwa yanzu an fara rarraba kayan a jihohin Naija da Bauchi Sokoto da Kano da Lagos.
Ana raba kayan ne bisa taimakon jami’an ‘yan sanda.