Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata cibiyar kula da lafiya domin kula Falasɗinawa 2,000 da suka jikkata lokacin yaƙin Gaza.
Wani mai magana da yawun gwamnati Hasan Nasbi ya musanta cewa shirin ba wai na kwashe Falasɗinawa bane.
Ya ce da zarar waɗanda ake kula da su a asibitin da ke Galang sun warke, za su koma Gaza.
Yankin Galang, wanda ke kusa da Singapore, ya taɓa kasancewa wani sansanin ƴan gudun hijira na Majalisar ɗinkin duniya da kuma cibiyar kula da Corona.
Sai dai zuwa yanzu ba a tabbatar da yadda za a kai Falasɗinawa yankin ba.