Gwamnatin India ta kori wasu sojojin samanta uku daga aiki bayan sun harba makami mai linzami Pakistan bisa kuskure.
Lamarin da ya faru tun a watan Maris, ya janyo zaman dar-dar tsakanin kasashen biyu.
India ta bayyana takaicinta kan lamarin da ta kira a matsayin sakaci da aiki.
Pakistan dai ta gargadi India a kan ta shiga taitayinta tare da kare afkuwar irin wannan lamari.
Rundunar sojan saman India, cikin wata sanarwa, ta ce ta sallami jami’anta uku saboda harba makami mai linzamin da suka yi cikin Pakistan bisa kuskure.
Ta ce binciken da ta yi ya gano rashin nutsuwa a yayin aiki ne ya janyomafkuwar lamarin. In ji BBC.