Gwamnatin Indiya ta gayyaci shugaba Bola Ahmed Tinubu zuwa taron kasashen G20.
Taron ana yin shi duk shekara wanda aka fara tun lokacin da aka kafa shi a shekarar 2008 bayan rikicin kudi na duniya na 1997-1998.
Taron na G20 ya tattaro manyan kasashe masu mahimmancin tattalin arziki na duniya tare da mambobin da ke wakiltar kashi 85 na GDP na duniya, kashi 75 na cinikayyar kasa da kasa da kashi biyu bisa uku na al’ummar duniya.
Da yake magana kan shirin samun shugaba Tinubu ya halarci taron, babban kwamishinan Indiya a Najeriya, Amb. Shri G. Balasubramanian, ya ce an riga an bude hanyoyin sadarwa tsakanin kasashen biyu don halartar shugaba Tinubu.
“Don haka dangane da haka, muna sa ran mai girma Mista Bola Tinubu, shugaban kasar Nijeriya zai ziyarci kasar Indiya domin taron G20 mai zuwa. Taron da za a yi a Indiya a ranakun 9 da 10 ga watan Satumba na wannan shekara,” inji shi.
“Don haka wannan wani abu ne da muke aiki kafada da kafada da hukumomin Najeriya.
“Mun yi tarurruka sama da 140 daga watan Disamba zuwa yanzu kuma mun gamsu sosai da halartar Najeriya a taron G20 da kuma a matakin ministoci, matakin kungiyar aiki, matakin rukuni, da dai sauransu.”
Membobin G20 sun hada da: Argentina, Australia, Brazil, Canada, China, Faransa, Jamus, Indiya, Indonesia, Italiya, Japan, Jamhuriyar Koriya, Mexico, Rasha, Saudi Arabia, Afirka ta Kudu, Turkiyya, Burtaniya, Amurka, da Tarayyar Turai.
Taron G20 ya zo a Indiya tsakanin 9 zuwa 10 ga Satumba, 2023.