fidelitybank

Ina zargin Gwamnatin Ganduje da ɗaukar nauyin Ƴan Daba a Kano – Gwamna

Date:

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya zargi gwamnatin da ta gabace shi da ɗaukar nauyin ‘yan daba a Kano.

Yayin da yake jawabi a gabanin taron majalisar zartarwar jihar da aka gudanar ranar Asabar a fadar gwamnatin jihar, Gwamnan Abba Kabir ya nuna damuwarsa kan halin taɓarɓarewar tsaro da jihar ke fuskanta, musamman harkar dabanci.

”Kowa ya sani kafin mu shigo gwamnati, waccan gwamnatin da ta shuɗe ita ce ke ɗaukar nauyin ‘yan daba, ita ce ke sa su suna yin abin da duk suka ga dama suna cutar da al’umma”, in ji gwamnan na Kano.

Gwamnan ya kuma ce a lokacin yaƙin neman zaɓensa ya yi alƙawarin kakkaɓe matsalar daba a Kano.

Ya kuma ce bayan nasararsa a zaɓen gwamnatinsa ta yi ƙoƙarin daƙile matsalar.

Amma ya ce a cikin wata biyu da suka gabata wasu da ya kira ”maƙiyan jihar” suka maido da harkar daba.

Inda ya yi zargin cewa wasu sun ɗauko hayar wasu ‘yan daba daga makwabtan jihohi domin su kawo wa zaman lafiyar jihar cikas.

Abba Kabir ya kuma yi barazanar fara kiran sunayen mutane da yake zargi da ɗaukar nauyin ‘yan daba a jihar.

Haka kuma gwamnan ya nuna damuwarsa kan yadda ya ce wasu na zuwa ofishin ‘yansanda domin fito da ‘yan daba idan hukuma ta kama su.

Inda ya yi barazanar cewa duk mutumin da gwamnatinsa ta sake samu da wannan laifi to za a gurfanar da shi a gaban kotu, domin yin bayanin dalilinsa na ɗaukar nauyin ‘yan daba a Kano.

A baya-bayan nan dai jihar Kano na fuskantar faɗace-faɗacen ‘yan daba, waɗanda ke cin karensu babu babbaka a wasu unguwannin jihar.

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp