fidelitybank

Ina zama shugaba zan cire tallafi man fetur – Tinubu

Date:

Dan takarar shugaban Ć™asa na jam’iyyar APC a zaben 2023, Bola Ahmed Tinubu, ya sha alwashin janye tallafin man fetur da zarar ya zama shugaban kasa.

Tinubu ya bayyana haka ne ranar Alhamis da daddare a yayin da yake gudanar da taro da wasu ‘yan kasuwa.

“Dokar man fetur tana nan kuma za mu duba ta a karo na biyu domin sauke nauyin da ke kanmu kuma duk zanga-zangar da za a yi, za mu cire tallafin man fetur,” in ji Tinubu.

Ya kara da cewa: “Za mu dauki matakai masu tsauri, wannan shi ne batun gaskiya. Don haka wajibi ne mu cire tallafin man fetur.”

Tinubu ya kara da cewa zai sanya kudin da ake biyan tallafin man fetur a fannonin da suka kamata irin su lafiya.

Kazalika ya ce zai cire jerin haraje-haraje da hukumomi suke karba yana ma cewa zai sa a rika karbar haraji daya kan mu’amalar da ta shafi a biya mata haraji.

Bayanai sun nuna cewa gwamnatin Najeriya ta biya N1.9 daga watan Janairu zuwa watan Yulin 2022 kadai, lamarin da wasu ke ganin ba abu ne mai dorewa ba.

Da ma dai shi ma dan takarar shugaban Najeriya na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya dade da shan alwashin janye tallafin man fetur idan ya zama shugaban kasa. Ya ce tallafin ba ya yi wa talakawa amfani.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ćłansanda

Kwamishinan Ć´ansanda mai kula da sashen kai É—auki na...

INEC za ta bai wa É—aurarru damar kaÉ—a Ć™uri’a a lokacin zaÉ“uka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

ĆŠaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon É—an takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaÉ—i mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaÉ—i...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp