fidelitybank

Ina yaƙi da masu ƙwacen filaye a Abuja ba ƙwace wa na ke yi ba – Wike

Date:

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya ce batun da ake yaɗawa cewa yana ƙwace filaye ba haka ba ne, inda ya ce yaƙi yake yi da masu ƙwace filaye, ba shi yake ƙwacen ba.

Wike ya bayyana haka ne a ranar Alhamis a wani taron da ƴan PDP na ƙaramar hukumar Ahoada ta Gabas na jihar Ribers, inda ya yi godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu bisa damar da ya ba shi, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Wike ya ce, “ina yaƙi ne da masu ƙwacen filaye. Wasu na cewa wai ƙwacen filaye ake yi, ta yaya za ka ƙwace filaye alhali kai ne ke da iko da filayen? ni nake da iko filaye a Abuja, to ta yaya zan ƙwace abun da nake da iko a kai?”

Ya ƙara da cewa yanzu ba kamar Rivers ba, da ƴan Najeriya baki ɗaya yake aiki, wanda hakan ya sa ƙara fahimtar wasu abubuwa.

“Wasu suna tunanin don ba a yi amfani da doka ba a baya, babu wanda zai zo ya yi. Amma ba haka ba ne, don wata gwamnati ba ta yi ba, hakan ba ya nufin babu gwamnatin ba za ta zo ta gyara. Don haka duk farfagandar da za a yi, ba za ta hana ni yin abubuwan da suka dace ba.”

www nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp