fidelitybank

Ina yaba wa ƴan Najeriya bisa amince wa Tinubu – Ganduje

Date:

Shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa, Dr. Abdullahi Ganduje, ya yabawa ‘yan Najeriya bisa goyon bayan da suka baiwa shugaba Bola Tinubu’s Renewed Hope Agenda.

A wata sanarwa da Ganduje ya fitar a ranar Lahadi a Abuja, ya taya al’ummar Musulmin Najeriya da ma duniya baki daya murnar zagayowar watan azumin Ramadan cikin nasara.

Ya jaddada kudirin gwamnatin da Tinubu ke jagoranta na inganta walwala da jin dadin daukacin ‘yan kasa, yana mai tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa ba za su yi nadamar zaben shugaban kasa ba a karshen wa’adinsa na farko.

Gwamna Ganduje ya yi bikin sabunta ruhi da tarbiyyar da aka samu a watan Ramadan, inda ya bukaci al’ummar Musulmi da su kiyaye dabi’un takawa, rashin son kai, da tausayi.

Ya kuma karfafa masu imani da su rika nuna kauna da kyautatawa juna, musamman ma marasa galihu.

Da yake jaddada mahimmancin hadin kai, zaman lafiya, da ci gaban kasa, shugaban jam’iyyar APC ya yi kira ga ‘yan kasa da su dage wajen samar da zaman lafiya da karfafa dimokuradiyyar kasar nan. Ya bayyana hakuri, sadaukarwa, da jajircewa – muhimman darussa na watan Ramadan – wadanda suke da muhimmanci ga ci gaban kasa.

Shugaban jam’iyyar APC ya bukaci Musulmi da ‘yan Najeriya baki daya da su ci gaba da yi wa Shugaba Tinubu addu’a domin samun nasara, inda ta bayyana fatan Allah (SWT) ya karbi addu’o’insu da sadaukarwarsu, ya kuma ba su albarkar da ke cikin wannan kakar.

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp