fidelitybank

Ina Tinubu ya ke ya ɓata ba bayani – ADC

Date:

Jam’iyyar African Democratic Congress wato ADC, ta soki Shugaba, Boa Tinubu, bisa abin da ta bayyana “ɓacewar kwana biyar ba tare da bayani ba” bayan ya halarci taron BRICS na 2025 a ƙasar Brazil.

Tinubu wanda ya halarci taron a birnin Rio de Janeiro da ke Brazil, ya koma ƙasar a ranar Lahadi, kwana biyar da kammala taron.

A wata sanarwa da kakakin jam’iyyar ADC, Bolaji Abdullahi ya fitar, ya ce babu wani bayani a hukumance da aka fitar game da kwana biyar ɗin da aka yi shugaban bai koma ba bayan kammala taron.

“ADC na ƙalubalantar Bola Tinubu ya bayyana wa ƴan Najeriya ina ya tsaya ya yi kwana biyar bayan kammala taron BRICS a Brazil,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

“Bayan kammala taron a ranar Litinin 7 ga watan Yuli, sauran shugabannin ƙasashen da suka halarta sun koma ƙasashensu, inda suka yi wa ƴan ƙasarsu bayanin abin da ya faru a can, sannan suka koma bakin aiki.

“Amma shugaban ƙasarmu fa? sai a ranar Lahadi 13 ga watan Yuli muka gan shi, kuma ba tare da wani bayanin me ya sa ya yi jinkirin dawowa ba.”

Bolaji ya ce kwana biyar na da matuƙar muhimmancin ganin yadda Najeriya ke fama da matsalar rashin tsaro da taɓarɓarewar tattalin arziki.

daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp