fidelitybank

Ina taya Tinubu Murna shugaban PDP ka yi murabus – Fayose

Date:

Peter Ayodele Fayose, tsohon gwamnan jihar Ekiti, yayi kira da shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu, ya yi murabus saboda gazawarsa wajen kai jam’iyyar zuwa mataki na gaba.

Fayose ya bayyana hakan ne jim kadan bayan ya taya zababben shugaban Najeriya, Bola Tinubu murnar nasarar da ya samu.

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, a safiyar Larabar da ta gabata ya ayyana Tinubu na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa na 2023.

Tinubu ya doke Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na jam’iyyar Labour inda ya zama wanda ya lashe zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar Asabar da ta gabata.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Laraba, Fayose ya ce, “Game da shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu, ina kira da ya gaggauta yin murabus saboda gazawarsa wajen ciyar da jam’iyyar gaba.

A baya Fayosed ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa, “Ina taya Asiwaju Bola Tinubu murnar zabar sa a matsayin shugaban kasar Najeriya. Ina kira ga sauran ’yan takara musamman Atiku Abubakar da su amince da sakamakon da aka samu domin amfanin kasarmu baki daya. Ko da yaushe za a sami wata rana.”

network news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp