Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya taya kasar Morocco murna bisa rawar ganin da ta yi na kasancewarta kasar Afirka ta farko ta kai wasan kusa da na karshe a gasar cin kofin duniya da ake a Qatar.
‘Yan wasan na Atlas Lions, sun doke kasashe kamar Belgium da Spaniya da kuma Portugal kafin su kai matakin da suke a yanzu.
Bisa irin rawar da suka taka a gasar cin kofin duniyar ya sa shugaban Najeriya Muhammadu ya yaba musu tare da cewa sun fitar da Afirka kunya, kuma irin kokarin da suka yi ya sanya fata a zukatan al’ummar nahiyar cewa za su iya daukar kofin.
Najeriya dai ba ta cikin kasashen Afirka biyar da suka buga wasa a gasar a wannan karon da ake bugawa a Qatar.
Mai magana da yawun shugaban kasar Malam Garba Shehu, ne ya wallafa sanarwar shugaban kasar a shafinsa na tiwita.