fidelitybank

Ina tare da ɗalibai masu sanya Hijabi – Gwamnan Kwara

Date:

Gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq, ya bayyana cewa, ko shakka babu ya na tare da ɗalibai mata Musulmai kan lamarin sanya Hijabi cikin makarantun jihar.

Gwamnan Ya ce, wannan ita ce matsayarsa, saboda shari’o’in da kotu ta yanke kan lamarin da kuma kasancewar Kwara jiha ce mai daidaito tsakanin addinai, kuma jihar da tafi kama da Kudu wajen adadin masu addinai mabananta.

Abdulrazaq ya kuma ce, gwamnatinsa kawai doka da gaskiya take bi da kuma nuna adalci tsakanin kowa, a tabakin sakataren yada labaransa, Rafiu Ajakaye, wanda ya bayyanawa Daily Trust.

Wannan jawabi na Gwamna ya biyo bayan tuhume-tuhumen da Musulmai da Kirista ke yi, cewa Gwamnan ya ki bayyana ra’ayinsa kan lamarin saboda siyasa.

Tuni dai iyalan Habeeb Idris, ɗalibar da aka kashe yayin zanga-zanga a makarantar Oyun Baptsit kwanakin baya, sun yi watsi da diyyar Naira miliyan 1 da gwamnatin jihar ta basu. Hakazalika mutum 11 da suka jikkata sun yi watsi da kuɗi Naira 250,000 da gwamnatin jihar ta basu.

nigerian 
newspapers today the sun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp