Gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq, ya bayyana cewa, ko shakka babu ya na tare da ɗalibai mata Musulmai kan lamarin sanya Hijabi cikin makarantun jihar.
Gwamnan Ya ce, wannan ita ce matsayarsa, saboda shari’o’in da kotu ta yanke kan lamarin da kuma kasancewar Kwara jiha ce mai daidaito tsakanin addinai, kuma jihar da tafi kama da Kudu wajen adadin masu addinai mabananta.
Abdulrazaq ya kuma ce, gwamnatinsa kawai doka da gaskiya take bi da kuma nuna adalci tsakanin kowa, a tabakin sakataren yada labaransa, Rafiu Ajakaye, wanda ya bayyanawa Daily Trust.
Wannan jawabi na Gwamna ya biyo bayan tuhume-tuhumen da Musulmai da Kirista ke yi, cewa Gwamnan ya ki bayyana ra’ayinsa kan lamarin saboda siyasa.
Tuni dai iyalan Habeeb Idris, ɗalibar da aka kashe yayin zanga-zanga a makarantar Oyun Baptsit kwanakin baya, sun yi watsi da diyyar Naira miliyan 1 da gwamnatin jihar ta basu. Hakazalika mutum 11 da suka jikkata sun yi watsi da kuɗi Naira 250,000 da gwamnatin jihar ta basu.