Kyaftin din kungiyar Al-Nassr, Cristiano Ronaldo, ya mayar da martani ga kungiyarsa ta Saudi Pro League da ta sha kashi a hannun Al Ittihad da ci 1-0 a ranar Alhamis.
Ronaldo ya kasa taimakawa Al-Nassr yayin da suka sha kashi a hannun Al Ittihad a filin wasanni na King Abdullah.
Romarinho ne ya zura kwallo daya tilo a wasan a minti na 80 da fara tamaula, inda ya farke da bugun daga kai sai mai tsaron gida.
Sakamakon hakan na nufin Al-Nassr yanzu maki daya ne a bayan shugabannin kungiyar Ittihad a teburin gasar Saudi Pro League.
Da yake mayar da martani, Ronaldo ya ce, ya ji takaicin sakamakon wasan.
Tsohon dan wasan na Manchester United ya kuma bukaci Al-Nassr da su mayar da hankali kafin wasannin da za su yi.
Ronaldo ya rubuta a shafinsa na Instagram cewa: “Na ji takaici da sakamakon, amma mun ci gaba da mai da hankali kan kakarmu da wasannin da ke gaba.
“Na gode wa magoya bayan Al Nassr, saboda goyon bayan ku, mun san za mu iya dogara da ku!”