fidelitybank

Ina takaici yadda wasu Matan ke shiga shaye-shaye a Kano – Sarki

Date:

Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya karbi bakuncin shugabar kungiyar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi, Ambasada Maryam Hassan a fadar sa.

Sarkin ya bayyana damuwarsa kan yadda shaye-shayen miyagun kwayoyi ke karuwa, musamman a tsakanin mata da matasa a cikin al’umma.

“Wasu daga cikin batutuwan da aka gabatar a gabanmu na da alaka da shaye-shayen miyagun kwayoyi; akwai ayyukan da ba za a iya aiwatarwa ba tare da shan kwayoyi ba, kamar mutum ya kashe dan uwansa ko iyayensa. Duk wannan ba zai iya faruwa ba sai idan mutum ya rasa hayyacinsa”. Ya kara da cewa

Khalifa Muhammadu Sanusi II ya bukace su da su mayar da hankali wajen wayar da kan al’umma, musamman kan illar shaye-shayen miyagun kwayoyi da ya zama ruwan dare gama gari.

A nata jawabin, shugabar kungiyar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi, Ambasada Maryam Hassan, ta bayyana cewa sun zo ne domin sanar da mai martaba irin ayyukan kungiyar musamman yaki da shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin al’umma musamman mata da matasa.

Ta ce, “Muna shirya taron karawa juna sani ga malamai da masu rike da mukaman gargajiya domin wayar da kan jama’a. Mun kuma gabatar da wata doka kan shaye-shayen miyagun kwayoyi ga Majalisar Dokoki ta kasa, amma har yanzu ba a gabatar da ita ba. Muna neman goyon bayan masarautar Kano don ganin an amince da kudirin a majalisar dokokin kasar.”

Bayan haka, Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, ya nada sabon Hakimin Kutama a karamar hukumar Gwarzo, Muhammad Murtala Safiyanu.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp