Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya karbi bakuncin shugabar kungiyar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi, Ambasada Maryam Hassan a fadar sa.
Sarkin ya bayyana damuwarsa kan yadda shaye-shayen miyagun kwayoyi ke karuwa, musamman a tsakanin mata da matasa a cikin al’umma.
“Wasu daga cikin batutuwan da aka gabatar a gabanmu na da alaka da shaye-shayen miyagun kwayoyi; akwai ayyukan da ba za a iya aiwatarwa ba tare da shan kwayoyi ba, kamar mutum ya kashe dan uwansa ko iyayensa. Duk wannan ba zai iya faruwa ba sai idan mutum ya rasa hayyacinsa”. Ya kara da cewa
Khalifa Muhammadu Sanusi II ya bukace su da su mayar da hankali wajen wayar da kan al’umma, musamman kan illar shaye-shayen miyagun kwayoyi da ya zama ruwan dare gama gari.
A nata jawabin, shugabar kungiyar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi, Ambasada Maryam Hassan, ta bayyana cewa sun zo ne domin sanar da mai martaba irin ayyukan kungiyar musamman yaki da shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin al’umma musamman mata da matasa.
Ta ce, “Muna shirya taron karawa juna sani ga malamai da masu rike da mukaman gargajiya domin wayar da kan jama’a. Mun kuma gabatar da wata doka kan shaye-shayen miyagun kwayoyi ga Majalisar Dokoki ta kasa, amma har yanzu ba a gabatar da ita ba. Muna neman goyon bayan masarautar Kano don ganin an amince da kudirin a majalisar dokokin kasar.”
Bayan haka, Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, ya nada sabon Hakimin Kutama a karamar hukumar Gwarzo, Muhammad Murtala Safiyanu.