fidelitybank

Ina takaici bisa yadda yunwa ke kashe ƴan Najeriya – Peter Obi

Date:

Kusan yara 40 ne suka mutu a wani hatsari yayin wani taron liyafar yara da aka shirya a Ibadan, babban birnin jihar Oyo, a ranar Laraba.

Haka zalika, a ranar Asabar, wani turmutsutsin ya faru a rabon tallafin a cocin Holy Trinity Catholic Church da ke unguwar Maitama a Abuja, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 10 tare da jikkatar wasu da dama.

A jihar Anambra, rahotanni sun bayyana cewa mutane kusan 17 a garin Okija yayin wani hatsari da ya faru a kokarin samun kayan tallafi.

Da yake tsokaci kan lamarin Obi ya bayyana takaicinsa a wata sanarwa da ya fitar ta dandalin sada zumunta na X. Ya ce hatsarurrukan sun nuna gazawar tsarin shugabanci da ke addabar Najeriya.

“Na yi matuƙar bakin ciki da damuwa kan asarar rayuka yayin neman abincin da zasu ci”

Obi ya yaba da ƙoƙarin masu shirya tarukan don tallafa wa talakawa amma ya bayyana cewa rashin ingantaccen tsarin tattalin arziki da shugabancin kasa ya sanya mutane cikin yanayin da ke jefa rayukansu cikin haɗari.

“Ya kamata a tambayi yadda ƙasa mai albarkatu irin Najeriya ta gagara ciyar da al’ummarta, duk da arzikin filayen noma da muke da su,” in ji shi.

Ya kuma mika ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda hatsarurrukan suka shafa. Obi ya ce, “ina mika ta’aziya ta ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu a Oyo, Anambra, da Abuja kuma ina fatan waɗanda suka jikkata su samu sauƙi cikin gaggawa.”

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp