Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ƙara tabbatarwa da al’ummar jihar Kaduna cewa, sojoji za su murƙushe ‘yan ta’adda da suka addabi jihar da sauran sassan kasar baki daya.
Buhari ya bayyana hakan ne a jiya Juma’a lokacin da ya je wata ziyarar bude ayyuka a jihar Kaduna.
Shugaba Muhammadu Buhari wanda ya jinjinawa jihar Kaduna, saboda goyon bayan da ta ke bai wa jami’an tsaro, ya nuna jin dadinsa ga yadda ta kada ma’aikatar tsaro ta cikin gida a jihar.
Ya ce, “Lokarin wannan gwamnatin ya janyo hankalin masu zuba jari daga kasashen waje suka zuba kudin da suka kai dalar Amurka biliyan 2.8 a jihar tun daga 2015”. A cewar Buhari.