Sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar gwamnan jihar a zaben 2023 mai zuwa.
Alhaji Usman ya ce, ya na son ya gaji Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ne a matsayin sa na gwamnati.
Wazirin Gaya ya bayyana aniyar sa ne a wajen liyafar cin abinci da kungiyar sa kai ta kishin kasa ta gudanar a Kano.
Ya kuma yi alkawarin yin gaskiya da gudanar da al’amuran jihar tare da tsoron Allah.
“Na yi niyyar dorawa kan kyakkyawan aikin Gwamna Ganduje, domin gwamnatina ta samu karbuwa kamar yadda yake faruwa a jihohin Legas da Kaduna da kuma Borno,” inji shi.