fidelitybank

Ina so Najeriya ta cigaba shi yasa na ke sauye-sauye a tattalin arziki – Tinubu

Date:

Shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya kare matakin sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatinsa ta ɗauka, inda ya ce, ya yi haka ne domin ƙasar ta samu ci gaba.

Shugaban ya bayyana haka ne ranar Juma’a a fadarsa da ke Abuja, lokacin da yake karɓar bakuncin jakada na musamman daga ƙasar Qatar, Dakta Mohammed bin Abdulaziz Al-Khulaifi.

Tinubu ya ce tsare-tsare da ake ɗauka na inganta harkar haraji a Najeriya, ya sa mutane daga ƙasashen waje na samun saukin zuba-jari da kuma kasuwanci a ƙasar.

“Muna ƙoƙari don inganta tsarin harajin mu. Wajibi ne mu ɓullo da sabbin tsare-tsare idan muka duba abubuwan da suka faru a baya na wahalhalu da aka fuskanta.

“Na ɗauki matakai masu tsauri saboda mu samu ci gaba. Sannu a hankali kwalliya za ta biya kuɗin sabulu,” in ji shugaban.

Ya ce za a inganta haɗin-kai tsakanin Najeriya da Qatar ne ta hanyar duba batun wadatar abinci da kuma ci gaban tattalin arziki.

“Ba za ka samu abokin hulɗa fiye da Najeriya ba. Na kasance ina bibiyar abubuwan da ke faruwa a duniya da kuma ƙoƙarinku. Ya kamata ku ƙara himma a Najeriya don yaƙi da talauci da kuma ayyuka jin-ƙai,” kamar yadda Tinubu ya faɗa wa jakadan na ƙasar Qatar.

benue news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp