fidelitybank

Ina so Najeriya ta cigaba shi yasa na ke sauye-sauye a tattalin arziki – Tinubu

Date:

Shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya kare matakin sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatinsa ta ɗauka, inda ya ce, ya yi haka ne domin ƙasar ta samu ci gaba.

Shugaban ya bayyana haka ne ranar Juma’a a fadarsa da ke Abuja, lokacin da yake karɓar bakuncin jakada na musamman daga ƙasar Qatar, Dakta Mohammed bin Abdulaziz Al-Khulaifi.

Tinubu ya ce tsare-tsare da ake ɗauka na inganta harkar haraji a Najeriya, ya sa mutane daga ƙasashen waje na samun saukin zuba-jari da kuma kasuwanci a ƙasar.

“Muna ƙoƙari don inganta tsarin harajin mu. Wajibi ne mu ɓullo da sabbin tsare-tsare idan muka duba abubuwan da suka faru a baya na wahalhalu da aka fuskanta.

“Na ɗauki matakai masu tsauri saboda mu samu ci gaba. Sannu a hankali kwalliya za ta biya kuɗin sabulu,” in ji shugaban.

Ya ce za a inganta haɗin-kai tsakanin Najeriya da Qatar ne ta hanyar duba batun wadatar abinci da kuma ci gaban tattalin arziki.

“Ba za ka samu abokin hulɗa fiye da Najeriya ba. Na kasance ina bibiyar abubuwan da ke faruwa a duniya da kuma ƙoƙarinku. Ya kamata ku ƙara himma a Najeriya don yaƙi da talauci da kuma ayyuka jin-ƙai,” kamar yadda Tinubu ya faɗa wa jakadan na ƙasar Qatar.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

Arziƙin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...
X whatsapp