fidelitybank

Ina so Najeriya ta cigaba shi yasa na ke sauye-sauye a tattalin arziki – Tinubu

Date:

Shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya kare matakin sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatinsa ta ɗauka, inda ya ce, ya yi haka ne domin ƙasar ta samu ci gaba.

Shugaban ya bayyana haka ne ranar Juma’a a fadarsa da ke Abuja, lokacin da yake karɓar bakuncin jakada na musamman daga ƙasar Qatar, Dakta Mohammed bin Abdulaziz Al-Khulaifi.

Tinubu ya ce tsare-tsare da ake ɗauka na inganta harkar haraji a Najeriya, ya sa mutane daga ƙasashen waje na samun saukin zuba-jari da kuma kasuwanci a ƙasar.

“Muna ƙoƙari don inganta tsarin harajin mu. Wajibi ne mu ɓullo da sabbin tsare-tsare idan muka duba abubuwan da suka faru a baya na wahalhalu da aka fuskanta.

“Na ɗauki matakai masu tsauri saboda mu samu ci gaba. Sannu a hankali kwalliya za ta biya kuɗin sabulu,” in ji shugaban.

Ya ce za a inganta haɗin-kai tsakanin Najeriya da Qatar ne ta hanyar duba batun wadatar abinci da kuma ci gaban tattalin arziki.

“Ba za ka samu abokin hulɗa fiye da Najeriya ba. Na kasance ina bibiyar abubuwan da ke faruwa a duniya da kuma ƙoƙarinku. Ya kamata ku ƙara himma a Najeriya don yaƙi da talauci da kuma ayyuka jin-ƙai,” kamar yadda Tinubu ya faɗa wa jakadan na ƙasar Qatar.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp