fidelitybank

Ina roƙon kotu ta ba ni dama na shigar da ƙara a kan Tinubu – Atiku

Date:

Ɗan takarar jam’iyyar PDP a zaɓen shugaban ƙasar Najeriya na 2023, Atiku Abubakar, ya buƙaci kotun ƙolin ƙasar ta ba shi damar miƙa sabbin hujjoji a ci gaba da matakinsa na ƙalubalantar nasarar shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu.

Wata buƙata da lauyoyinsa suka gabatar, ta ce sabuwar shaidar da Atiku ke son gabatar wa kotun za ta tabbatar da zargin da yake yi kan cewa shugaba Tinubu ya yi amfani da takardun bogi a lokacin da yake ƙoƙarin ganin ya fafata a zaɓen shugaban ƙasa.

Atiku Abubakar ya ce wannan abu da Tinubu ya yi na nuna cewa ya aikata laifuka biyu, wato ƙirƙirar takardar kammala karatu ta bogi da kuma ƙarya.

A cewar Atiku waɗannan hujjoji sun ishi kotun ƙoli ta dogara da su wajen cire shugaban ƙasar daga muƙaminsa.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar na so ne kotu ta ba shi wannan dama domin ya miƙa mata takardun shaidar kammala karatun Bola Ahmed Tinubu, waɗanda jami’ar jihar Chicago da ke Amurka ta miƙa masa a ranar biyu ga watan Oktoba.

Bayanai dai sun nuna cewa Atiku ya shigar da buƙatar tasa ce a ranar Juma’ar da ta gabata.

Sai dai har yanzu kotun ba ta sa ranar da za ta yanke hukunci kan buƙatar ta Atiku ba.

Shi dai Atiku Abubakar yana ƙalubalantar nasarar da Bola Ahmed Tinubu ne ya samu a zaɓen shugaban Najeriya da aka gudanar cikin watan Fabarairun 2013.

A ranar 6 ga watan Satumba ne kotun sauraron ƙorafin zaɓen shugaban ƙasa ta tabbatar da nasarar Tinubu tare da yin watsi da hujjojin Atiku Abubakar na ja

vanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp