fidelitybank

Ina nan a PDP kuma ba zan marawa Atiku baya ba -Wike

Date:

Gwamnan jihar Ribas, Nyeson Wike, ya ce, zai ci gaba da zama a jam’iyyar PDP amma ya kawar da yiwuwar marawa da kuma yin aiki domin samun nasarar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Alhaji Atiku Abubakar.

Wani makusancin gwamnan ya shaidawa manema labarai a yau, 28 ga watan Yuli cewa ba zai koma jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki ba, duk da ci gaban da shugabannin jam’iyyar ke samu gabanin babban zaben 2023.

Gwamna Wike ya yi shiru kan zaben shugaban kasa da ke tafe biyo bayan koke-kokensa da tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku.

Hakan na zuwa ne bayan Gwamna Wike ya yi barazanar bayyana wa ‘yan Najeriya duk wani abu da ya faru a jam’iyyar PDP tun bayan fitowar Atiku a matsayin dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar.

Wike ya ce: “Akan Atiku, zan yi magana nan ba da jimawa ba, kuma ‘yan Najeriya za su san gaskiyar duk abin da ya faru a PDP a ‘yan kwanakin nan.”

Sai dai Atiku ya ce kwamitin da gwamnan jihar Binuwai, Samuel Ortom ya jagoranta ya ba shi sunaye guda uku kawai ya yanke shawarar zabar wadanda zai yi aiki da su.

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya zabi gwamnan jihar Delta, Ifeanyi Okowa a matsayin mataimakinsa.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp