fidelitybank

Ina nan a kan kujera ta ban yi murabus ba – Mataimakin Gwamna

Date:

Mataimakin gwamnan jihar Bauchi, Sanata Baba Tela, ya karyata rade-radin da ake yadawa a jihar cewa, ya yi murabus daga mukaminsa.

Baba Tela yana mayar da martani ne a kan wasu labaran da aka wallafa a shafukan sada zumunta cewa, ya ajiye mukaminsa na mataimakin gwamnan jihar Bauchi.

A cewarsa, har yanzu yana kan mukamin mataimakin gwamnan jihar Bauchi.”

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na ofishin mataimakin gwamna Sani Mu’azu Ilellah ya raba wa manema labarai a Bauchi.

“An jawo hankalin mataimakin gwamnan jihar Bauchi Sen. Baba Tela kan labaran karya a shafukan sada zumunta cewa, mataimakin gwamnan ya yi murabus daga mukaminsa. Bayanin rahoton da ake yi a kafafen sada zumunta na zamani, kwatankwacin tunanin marubuci ne.”

“Don kauce wa shakku, muna so mu tabbatar wa al’ummar Jihar Bauchi masu son zaman lafiya da himma, musamman ma kasa baki daya, cewa Sanata Bala Tela bai yi murabus daga mukaminsa na Mataimakin Gwamnan Jihar Bauchi ba.”

“Mai girma mataimakin gwamna, ya ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da manufofi da manufofin gwamnatin jihar Bauchi a karkashin ingantacciyar jagorancin mai girma Sanata Bala Abdulkadir Mohammed.” Sanarwar ta kara da cewa a sassa daban-daban.

Yayin da yake jaddada goyon bayansa da biyayya ga gwamnan, Baba Tela ya gargadi masu yada jita-jita da ke da niyyar haddasa rashin jituwa a jihar da su guji irin wannan aika aika.

tribune news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...
X whatsapp