fidelitybank

Ina nadamar siya wa marigayi Janar Lagbaja fom ɗin shiga soja – Kawunsa

Date:

Shugaban iyalan gidan su tsohon babban hafsan sojin ƙasa na Najeriya, Laftana Janar Taoreed Lagbaja, Pa Tajudeen Lagbaja, ya ce ya yi nadamar saya wa marigayin takardar neman shiga makarantar horad da ƙananan hafsoshin sojan Najeriya, (NDA).

Pa Tajudeen, wanda ƙani ne ga mahaifin marigayin ya ce da ya san hakan zai kai ga rasuwar Janar Lagbaja da tun da farko bai sai masa fom ɗin ba.

Haka kuma wasu dangi ko iyalan marigayin sun yi zargin cewa wataƙila an kashe Laftana Janar Lagbaja ne ta wata muguwar hanya saboda rikicin wani fili a garinsu.

Jaridar Daily Trut ta ruwaito cewa jaridar The Nation, ta bayar da labarin cewa a 2023 wani rikici ya tashi a garin Ilobu, hedikwatar ƙaramar hukumar Irepodun da ke jihar Osun, a lokacin da wakilan rundunar sojin ƙasa ta Najeriya suka shirya gina asibiti a garin.

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa marigayi Lagbaja a matsayin babban hafsan sojin ƙasar a watan Yuni na 2023,inda ya maye gurbin Laftanar Janar Faruk Yahaya, wanda tsahon shugaban Najeriyar Muhammadu Buhari ya naɗa a 2021.

Rahotanni sun ce tun bayan ba shi muƙamin, ya riƙa fama da rashin lafiyar da take kawo masa tsaiko wajen gudanar da aikinsa, lamarin da ke sanyawa yana yawan fita ƙasashen ƙetare neman magani.

Gwamnatin Najeriya ta fitar da sanarwa cewa babban hafsan sojin na ƙasa ya rasu ranar 5 ga watan nan na Nuwamba, 2024, yana da shekara 56 a wani asibiti a Lagos, bayan ya sha fama da rashin lafiyar da ba a bayyana ba.

sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp