fidelitybank

Ina nadamar siya wa marigayi Janar Lagbaja fom ɗin shiga soja – Kawunsa

Date:

Shugaban iyalan gidan su tsohon babban hafsan sojin ƙasa na Najeriya, Laftana Janar Taoreed Lagbaja, Pa Tajudeen Lagbaja, ya ce ya yi nadamar saya wa marigayin takardar neman shiga makarantar horad da ƙananan hafsoshin sojan Najeriya, (NDA).

Pa Tajudeen, wanda ƙani ne ga mahaifin marigayin ya ce da ya san hakan zai kai ga rasuwar Janar Lagbaja da tun da farko bai sai masa fom ɗin ba.

Haka kuma wasu dangi ko iyalan marigayin sun yi zargin cewa wataƙila an kashe Laftana Janar Lagbaja ne ta wata muguwar hanya saboda rikicin wani fili a garinsu.

Jaridar Daily Trut ta ruwaito cewa jaridar The Nation, ta bayar da labarin cewa a 2023 wani rikici ya tashi a garin Ilobu, hedikwatar ƙaramar hukumar Irepodun da ke jihar Osun, a lokacin da wakilan rundunar sojin ƙasa ta Najeriya suka shirya gina asibiti a garin.

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa marigayi Lagbaja a matsayin babban hafsan sojin ƙasar a watan Yuni na 2023,inda ya maye gurbin Laftanar Janar Faruk Yahaya, wanda tsahon shugaban Najeriyar Muhammadu Buhari ya naɗa a 2021.

Rahotanni sun ce tun bayan ba shi muƙamin, ya riƙa fama da rashin lafiyar da take kawo masa tsaiko wajen gudanar da aikinsa, lamarin da ke sanyawa yana yawan fita ƙasashen ƙetare neman magani.

Gwamnatin Najeriya ta fitar da sanarwa cewa babban hafsan sojin na ƙasa ya rasu ranar 5 ga watan nan na Nuwamba, 2024, yana da shekara 56 a wani asibiti a Lagos, bayan ya sha fama da rashin lafiyar da ba a bayyana ba.

latest news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp