fidelitybank

Ina nadamar siya wa marigayi Janar Lagbaja fom ɗin shiga soja – Kawunsa

Date:

Shugaban iyalan gidan su tsohon babban hafsan sojin ƙasa na Najeriya, Laftana Janar Taoreed Lagbaja, Pa Tajudeen Lagbaja, ya ce ya yi nadamar saya wa marigayin takardar neman shiga makarantar horad da ƙananan hafsoshin sojan Najeriya, (NDA).

Pa Tajudeen, wanda ƙani ne ga mahaifin marigayin ya ce da ya san hakan zai kai ga rasuwar Janar Lagbaja da tun da farko bai sai masa fom ɗin ba.

Haka kuma wasu dangi ko iyalan marigayin sun yi zargin cewa wataƙila an kashe Laftana Janar Lagbaja ne ta wata muguwar hanya saboda rikicin wani fili a garinsu.

Jaridar Daily Trut ta ruwaito cewa jaridar The Nation, ta bayar da labarin cewa a 2023 wani rikici ya tashi a garin Ilobu, hedikwatar ƙaramar hukumar Irepodun da ke jihar Osun, a lokacin da wakilan rundunar sojin ƙasa ta Najeriya suka shirya gina asibiti a garin.

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa marigayi Lagbaja a matsayin babban hafsan sojin ƙasar a watan Yuni na 2023,inda ya maye gurbin Laftanar Janar Faruk Yahaya, wanda tsahon shugaban Najeriyar Muhammadu Buhari ya naɗa a 2021.

Rahotanni sun ce tun bayan ba shi muƙamin, ya riƙa fama da rashin lafiyar da take kawo masa tsaiko wajen gudanar da aikinsa, lamarin da ke sanyawa yana yawan fita ƙasashen ƙetare neman magani.

Gwamnatin Najeriya ta fitar da sanarwa cewa babban hafsan sojin na ƙasa ya rasu ranar 5 ga watan nan na Nuwamba, 2024, yana da shekara 56 a wani asibiti a Lagos, bayan ya sha fama da rashin lafiyar da ba a bayyana ba.

nnn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp