fidelitybank

Ina miƙa ta’azziya ga iyalan mutanen da suka rasa rayukansu yayin Zanga-zanga – Peter Obi

Date:

Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party, LP, Mista Peter Obi, ya jajanta wa wadanda suka rasa rayukansu a zanga-zangar #Endbad-badad mulki da aka kammala a kasar.

Da yake mika sakon ta’aziyya ga iyalan da suka yi rashi a gwagwarmayar, Obi ya ce, marigayin sun sadaukar da rayuwarsu ne yayin da suke fafutukar ganin an samar da ingantaccen shugabanci a kasar.

A cikin sakonsa na X a ranar Lahadi, tsohon gwamnan jihar Anambra ya ce, magance matsalar rashin tsaro, yaki da cin hanci da rashawa, rage wahalhalu, da yaki da fatara, lamari ne na gaggawa da ke bukatar kulawa cikin gaggawa.

Don haka ya yi kira ga dukkan shugabanni da su dauki kwakkwaran mataki don warware wadannan muhimman batutuwa.

Obi ya ce: “Tare da zanga-zangar #Endbad mulki da aka kammala jiya a hukumance, ina so in sake jajanta wa duk wadanda suka rasa rayukansu ciki har da jami’an tsaro yayin wannan zanga-zangar.

“Wadannan mutane sun sadaukar da rayuwarsu ne a lokacin da suke fafutukar ganin an kyautata shugabanci a kasarmu. Ina mika sakon ta’aziyyata ga daukacin iyalai da suka yi asara a wannan gwagwarmaya. Dukkanmu muna tare da ku cikin bakin ciki, yayin da muke aiki tare don ci gaban kasarmu.

“Bari mu sami ƙarfin jure wannan rashin da ba za a iya maye gurbinsa ba. Ga wadanda suka samu raunuka kuma suna samun sauki a asibitoci da kuma a gida, ku sani cewa tunaninmu da addu’o’inmu suna tare da ku don samun sauki cikin gaggawa. Muna matukar godiya da sadaukarwar da kuka bayar ga al’ummarmu.

“Har ila yau, ina so in dauki wannan lokacin don kira ga dukkan shugabanni da su yi tunani kan kukan mutanen da ke cikin wahala tare da magance halalcin bukatunsu. Yana da mahimmanci a gare mu, shugabanni, mu yi gaggawar magance matsalolin da suka haifar da rura wutar zanga-zangar.

“Maganin rashin tsaro, yaki da cin hanci da rashawa, rage wahalhalu, da yaki da fatara, al’amura ne na gaggawa da ke bukatar kulawa cikin gaggawa. Ina kira ga dukkan shugabanni da su dauki kwakkwaran mataki don warware wadannan muhimman batutuwa.

“Allah ya sa wanda ya rasu ya huta lafiya, kuma wadanda suka jikkata kuma su samu sauki cikin gaggawa.

Sabuwar Najeriya ta kasance mai yiwuwa. – PO”

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp