Shugaban Jam’iyyar APC na kasa, Dr Abdullahi Ganduje, ya mika ta’aziyyata bisa rasuwar darakta masana’antar Kannywood Aminu Surajo Bono.
A cikin wata sanarwa da mai yada labaransa, Edwin Olofu, ya fitar ranar Talata, Dr Ganduje ya ce ya kadu matuka bayan samu labarin rasuwar wannan shararran darakta.
Ganduje wanda ya ce rasuwar Darakta Aminu Surajo Bono ba kamaramin rashi ba ne ga masana’antar Kannywood, ya kara da cewa rasuwar daraktan ta bar babban gibi a masana’antar.
Shugaban jam’iyyar ya kara da cewa Darakta Aminu Surajo Bono ya yi amfani da lokacinsa wajen bunkasa masana’antar Kannywood ta hanaya gudanar da tsaftacacciyar rayuwa.
Ganduje ya ce, “Na kadu matuka da samun labarin rasuwar Darakta Aminu Surajo Bono. Wannan ba rashi ba ne kawai ga masana’antar Kannywood ba. Babban rashi ne ga al’umma.
“Ina amfani da wannan dama dan mika ta’aziyya ga iyalansa da ‘yan uwansa da masana’antar Kannywood. Ina rokon Allah ya basu juriyar wannan rashi.
“Tabbas Darakta Aminu Surajo Darakta Aminu Surajo a cikin finafinai da kuma zahiri abar yabawa ce.”
Dr Abdullahi Ganduje ya ce ya na rokon Allah (SWT) da ya bawa iyalansa da masana’antar kannywood juriyar wannan baban rashi, ya na mai rokon Allah (SWT) da ya gafarta matawa mamacin.