Tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya bayyana alhininsa game da mutanen da ‘yanbindiga suka kashe a jihar Yobe a farkon makon nan.
Wata sanarwa da Garba Shehu, mai magana da yawunsa, ya wallafa a shafukan zumunta ta ce harin na baya-bayan nan “mummunar tunatarwa ce ga mazauna yankuna cewa akwai babban aiki a gabansu da za su yi wajen taimakawa a daÆ™ile matsalar ‘yanta’adda”.
Rahotonni daga jihar ta Yobe da ke arewa maso gabashin Najeriya na cewa an yi jana’izar mutum 30 da maharan masu iÆ™irarin jihadi suka kashe.
Cikin saÆ™on da ya aika wa Gwamna Mai Mala Buni da kuma majalisar sarakunan Yobe, tsohon shugaban ya yi addu’ar Allah ya ji Æ™an su, in ji sanarwar.
“Ya kuma nemi a É—auki mummunan mataki kan waÉ—anda suka aikata wannan aikin rashin imanin.”