Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Litinin, ya samu labarin kisan wasu alhazan Najeriya musulmi da aka yi a kan hanyarsu ta zuwa birnin Kaolack na kasar Senegal, lokacin da motocin bas din da ke dauke da su suka fuskanci harin bindiga a Burkina Faso.
Buhari ya jajanta musu tare da addu’ar Allah ya jikan sauran ‘yan Najeriya da suka makale a wurin.
An bayyana hakan ne a wata sanarwa da mai taimaka wa Buhari kan harkokin yada labarai, Garba Shehu, ya fitar a ranar Litinin.
Karanta Wannan:Â Gwamnoni uku sun kai karar Buhari zuwa kotu
A cewarsa, ma’aikatar harkokin wajen kasar ta hannun ofishin jakadancin Najeriya dake Burkina Faso, tana tattaunawa da mahukuntan Burkina Faso, tare da jiran sakamakon binciken da suka gudanar kan wannan lamari mara dadi, kuma idan ya zama dole, don tabbatar da cewa an hukunta dukkan masu laifi yadda ya kamata.
Ya kara da cewa gwamnatin tarayyar Najeriya za ta yi duk mai yiwuwa wajen ganin an ceto gawarwakin wadanda suka mutu da kuma wadanda suka tsira daga harin.