Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, yayi ta’aziyya ga Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa bisa rasuwar ɗansa na fari, Abdulwahab Umar Namadi, wanda ya rasu sakamakon haɗarin mota.
A wata sanarwa da Sakataren labaran gwamna, Sunusi Bature, ya fitar a ranar Alhamis, Gwamna Yusuf ya bayyana lamarin a matsayin “babban rashi ba kawai ga iyalan Namadi ba, amma ga gwamnatin Jihar Jigawa da yankin baki ɗaya.”
A cewar gwamnan: “Wannan wani lokaci ne mai cike da baƙin ciki ga al’ummar Jihar Jigawa. Ina roƙon Allah Madaukaki Ya ba Abdulwahab hutawa har abada a Jannatul Firdaus, kuma Ya ba iyalan Namadi da al’ummar Jigawa hakuri da ƙarfin zuciya a wannan lokacin alhini.”
Abdulwahab, wanda yake da shekaru 24, ya rasu ne sakamakon haɗarin mota a hanyarsu ta dawowa daga Kafin Hausa tare da abokansa, kwana guda bayan rasuwar Kakarsa.
Shi kaɗai ne ya rasa ransa a haɗarin, yayin da abokinsa ke samun kulawa a asibiti.
Gwamna Namadi, wanda ke kasar Sin a halin yanzu don wata ziyara ta aiki, na ci gaba da samun sakonnin ta’aziyya daga ‘yan uwa, abokan aiki, da shugabanni.