fidelitybank

Ina miƙa saƙon ta’azziya ga Gwamna Jigawa bisa mutuwar Babban Ɗansa – Gwamnan Kano

Date:

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, yayi ta’aziyya ga Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa bisa rasuwar ɗansa na fari, Abdulwahab Umar Namadi, wanda ya rasu sakamakon haɗarin mota.

A wata sanarwa da Sakataren labaran gwamna, Sunusi Bature, ya fitar a ranar Alhamis, Gwamna Yusuf ya bayyana lamarin a matsayin “babban rashi ba kawai ga iyalan Namadi ba, amma ga gwamnatin Jihar Jigawa da yankin baki ɗaya.”

A cewar gwamnan: “Wannan wani lokaci ne mai cike da baƙin ciki ga al’ummar Jihar Jigawa. Ina roƙon Allah Madaukaki Ya ba Abdulwahab hutawa har abada a Jannatul Firdaus, kuma Ya ba iyalan Namadi da al’ummar Jigawa hakuri da ƙarfin zuciya a wannan lokacin alhini.”

Abdulwahab, wanda yake da shekaru 24, ya rasu ne sakamakon haɗarin mota a hanyarsu ta dawowa daga Kafin Hausa tare da abokansa, kwana guda bayan rasuwar Kakarsa.

Shi kaɗai ne ya rasa ransa a haɗarin, yayin da abokinsa ke samun kulawa a asibiti.

Gwamna Namadi, wanda ke kasar Sin a halin yanzu don wata ziyara ta aiki, na ci gaba da samun sakonnin ta’aziyya daga ‘yan uwa, abokan aiki, da shugabanni.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp