Shahararren dan wasan barkwanci na Najeriya, Lasisi Elenu, ya janyo ce-ce-ku-ce a shafukan sada zumunta bayan da ya nuna kishinsa ga tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Dangane da halin kuncin da kasar nan ke ciki, dan wasan barkwancin ya ce ya yi kewar Buhari.
Lasisi ya shahara da irin abubuwan ban dariya da ya yi kan al’amuran al’umma daban-daban.
Kalaman da ya yi game da Buhari sun tayar da raha da tunani a tsakanin mabiyansa.
Shahararren dan wasan barkwanci, wanda ainahin sunansa Nosa Afolabi, ya shiga shafin Instagram a ranar Laraba inda ya raba faifan muryar da ya aikewa tsohon shugaban kasar a matsayin sako na sirri inda ya kusa hawaye yana kewarsa.
A cikin bayanin muryar, ya ce: “Ba na aiko muku da wannan sakon a madadin kowa ba. Ina tsammanin ina bin kaina da iyalina bashin. Ban taba tunanin zan kasance a nan ina yin wannan a wannan lokacin ba. Na farko, ban ma san yadda zan faÉ—i wannan ba. Ina kewar ku Allah ya taimakeni kada in mutu”
Ku tuna cewa Buhari ya bar mulki a watan Mayun 2023, kuma tun lokacin, yawancin ‘yan Najeriya sun yi imanin al’amura sun tabarbare ta fuskar tattalin arzikin kasar.
Rubutun É—an wasan barkwanci ya haifar da raÉ—aÉ—i iri-iri akan layi.
Wasu magoya bayansa sun amince da ra’ayinsa, inda suka ce lokacin da Buhari ya yi mulki ya samar da tsari, yayin da wasu ke nuna kalubalen da aka fuskanta a lokacin shugabancinsa.