Gwamna jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya sake nanata kiransa ga gwamnatin tarayyar cewa, ta dauko sojojin haya daga kasashen waje, domin taimakawa wajen murkushe kungiyoyin ‘yan tayar da kayar baya.
Gwamna Zullum ya jaddada hakan ne, a shugaban kasa da ke Abuja yayin wani taron manema labarai kan irin ci gaban da ake samu wajen yaki da kungiyoyin Boko Haram da ISWAP a jiharsa.
Ko a bara ma dai gwamnan ya yi irin wannan kiran, amma gwamnatin kasar ta kawar da yiwuwar bin wannan shawarar.