fidelitybank

Ina jin takaici duhun da Arewa ke fama na rashin wutar lantarki – Tinubu

Date:

Shugaba Bola Tinubu ya nuna damuwarsa kan rashin wutar lantarki da Arewacin ƙasar nan ke ci gaba da fuskanta.

Wata sanarwa da mai bai wa shugaban shawara kan harkar yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya fitar, ya ce abin damuwa ne matuka ganin yadda ƴan yankin ke ci gaba da kasancewa cikin duhu kuma hakan na ƙara kassara ɓangaren tattalin arziki.

Tinubu ya ce yanzu yana jagorantar ƙoƙari da ake yi wajen ganin an gyara matsalar ta rashin lantarki.

Ya buƙaci ministan lantarki da sauran hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta kammala aikin gyara turakun wuta da aka lalata da nufin mayar da wuta ga jihohin arewa.

“Ina cikin damuwa ainun kan rahotannin lalata wayoyin lantarki da sauran abubuwa da suka janyo rahin wuta,” in ji Tinubu.

Tinubu ya yi kira ga kamfanin rarraba wutar lantarki na Najeriya da su ƙoƙarta wajen ganin lantarki ta koma domin rage wa al’uma raɗadin da suke ciki.

Ya ce gwamnati ba za ta lamunci ci gaba da yin zagon ƙasa da kuma lalata turakun wutar lantarki ba.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp