Shugaban kungiyar gwamnonin Kudu kuma gwamnan jihar Ogun, Prince Dapo Abiodun, ya jajanta wa takwaransa na jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, da al’ummar jihar kan lamarin ambaliyar ruwa da ta afku a Maiduguri, babban birnin jihar kwanan nan.
Gwamnan, a wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai da dabaru, Hon. Kayode Akinmade, ya ce ambaliyar ruwan ta haifar da munanan matsalolin jin kai a jihar, wanda ke bukatar tallafin gaggawa daga dukkan ‘yan Najeriya masu kishin kasa.
Ya ce, “yayin da bala’o’in da ke faruwa a wannan yanayi ba su da makawa, daukar matakin gaggawa irin na gwamnatin Borno da na gwamnatin tarayya zai taimaka matuka wajen daidaita lamarin da kuma kawo dauki ga jama’a cikin gaggawa.”
“Ina mika ta’aziyya ga dan uwana Farfesa Babagana Zulum da al’ummar Jihar Borno bisa mummunar ambaliyar ruwa da ta afku a Jihar, wanda ya haifar da matsalar jin kai mai girman gaske.
“Gwamnati da al’ummar jihar Ogun na tare da Borno a wannan lokaci na kunci kuma za mu ci gaba da yi musu addu’a,” in ji sanarwar.