fidelitybank

Ina jajantawa gwamnan Borno da al’ummarsa – Abiodun

Date:

Shugaban kungiyar gwamnonin Kudu kuma gwamnan jihar Ogun, Prince Dapo Abiodun, ya jajanta wa takwaransa na jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, da al’ummar jihar kan lamarin ambaliyar ruwa da ta afku a Maiduguri, babban birnin jihar kwanan nan.

Gwamnan, a wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai da dabaru, Hon. Kayode Akinmade, ya ce ambaliyar ruwan ta haifar da munanan matsalolin jin kai a jihar, wanda ke bukatar tallafin gaggawa daga dukkan ‘yan Najeriya masu kishin kasa.

Ya ce, “yayin da bala’o’in da ke faruwa a wannan yanayi ba su da makawa, daukar matakin gaggawa irin na gwamnatin Borno da na gwamnatin tarayya zai taimaka matuka wajen daidaita lamarin da kuma kawo dauki ga jama’a cikin gaggawa.”

“Ina mika ta’aziyya ga dan uwana Farfesa Babagana Zulum da al’ummar Jihar Borno bisa mummunar ambaliyar ruwa da ta afku a Jihar, wanda ya haifar da matsalar jin kai mai girman gaske.

“Gwamnati da al’ummar jihar Ogun na tare da Borno a wannan lokaci na kunci kuma za mu ci gaba da yi musu addu’a,” in ji sanarwar.

the nation newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp