Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya jajanta wa iyalan mutanen da suka yi asarar rayuka a Sabon Gari, Kano, sakamakon fashewar tukunyar iskar gas a ranar Talata, inda aka samu asarar rayuka tara, ya kuma umurci jami’ai da su ba da isassun magunguna ga wadanda suka jikkata.
“Fashewar tukunyar iskar gas a Kano abin bakin ciki ne. Ina mika ta’aziyyata ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu. Ina yi wa wadanda suka jikkata fatan samun sauki cikin gaggawa,” in ji shugaban, a cewar wata sanarwar manema labarai da kakakinsa Garba Shehu ya fitar.
Ya kara da cewa, “A wannan lokaci na bakin ciki, ina rokon Allah Madaukakin Sarki da Ya karawa iyalan wadanda abin ya shafa juriya, gwamnati da al’ummar Jihar Kano tare da rokonsu da su dauki nauyin wannan rashi da ba za a iya kwatantawa ba.”
Shugaba Buhari ya yaba da matakin gaggawa da hukumomin gwamnatin jihar, da hukumar bada agajin gaggawa ta NEMA, da sojoji, da ‘yan sanda da sauran hukumomin gwamnatin tarayya.