Daraktan Kudi na Hukumar Raya Kogin Hadeja-Jama’are, Musa Iliyasu Kwankwaso, ya bayyana goyon bayansa na ganin an sasanta tsakanin tsaffin gwamnonin Jihar Kano—Kwankwaso, Ganduje, Shekarau, da Kabiru Gaya.
“Hakika hada wadannan mutane wuri guda domin sulhu zai taimaka wajen ci gaban jihar Kano, abin da al’ummar jihar za su yi alfahari da shi. Don haka samar da zaman lafiya a tsakaninsu mataki ne mai kyau,” inji shi.
Ya bayyana haka ne a wata hira da Kadaura24 a ranar Laraba.
Ya koka da koma bayan da Kano ta samu sakamakon koma-bayan ayyukan alfanu da gwamnati daya ta fara, duk da tasirin da suke da shi ga al’umma.
“Muna son tsaffin gwamnoni su hada kai wajen yanke shawarwarin da za su inganta rayuwar al’umma kuma su amince cewa duk wani aiki da za a yi don amfanin jama’a bai kamata a soke shi ba saboda sabanin siyasa,” inji shi.
Ya kuma kara da cewa duk tsaffin gwamnonin sun haura shekaru 65 a yanzu, wanda hakan ya sa ya dace su hada kai domin ci gaban jihar Kano.