fidelitybank

Ina godiya ga Tinubu bisa fara aiki a matata ta fetur – Dangote

Date:

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya miƙa saƙon godiyarsa ga shugaban Najeriya Bola Tinubu kan goyon bayan da ƙwarin gwiwa da kuma shawarwarin ya ba shi wajen fara aikin matatar man fetur ɗin da ya gina.

A ranar Juma’a ne matatar tara aikin tace iskar gas da kuma man jirgi.

Matatar da ta laƙume dala biliyan 19 wajen aikin gina ta, za ta riƙa tace ganga 650,000 a kowace rana, za ta yi ƙoƙarin kawar da matsalar karancin man fetur da Najeriya ke fuskanta.

Dangote ya kuma gode wa kamfanin mai na ƙasar NNPC da hukummomin kula da sarrafa albarkatun man fetur na ƙasar NUPRC da NMDPRA da kuma ‘yan Najeriya bisa goyon bayan da suka ba shi don tabbatar da fara aikin matatar.

Yayin da yake bayyana matatar a matsayin ”mai sauya lamura”, Dangote ya ce a yanzu matatar za ta riƙa tace ganga 350,000 a kowace rana kafin baya baya ta riƙa tace abin da aka tsara tun farko.

Matatar ta tara gangar mai miliyan shida kafin ta fara aikin tacewar.

Sabuwar matatar- wadda aka kwashe kusan shekara bakwai ana ginata – za ta iya loda wa manyan motocin dakon mai 2,900 a kowace rana.

Ana ganin fara aikin matatar zai taimaka matuƙa wajen wadata Najeriya da man fetur, har ma ta zama ƙasa mafi fitar da tataccen man fetur.

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp