Tsohon ƙaramin ministan gidaje na Najeriya, Abdullahi Tijjanai Gwarzo ya yaba wa shugaban ƙasar Bola Tinubu bisa damar da ya ce ya ba shi na hidimta wa ƙasar.
Gwarzo na cikin jerin ministoci biyar da shugaba Tinubu ya sanar da sallamarsu daga aiki a ranar Laraba, a wani garambawul a majalisar ministocin ƙasar.
A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, tsohon ministan ya ce shekara guda da ya yi a matsayin, ya mayar da hankalinsa wajen magance matsalar gidaje a ƙasar da inganta birane.
Tsohon ministan ya kuma ce a ɗan taƙaitaccen lokacin da ya yi a matsayin, yana alfahari da irin gudunmowar da ya bayar tare da gode wa shugaban ƙasar.
”Ina miƙa godiyata ga shugaban ƙasa bisa amincewar da ya yi da ni, har ya ba ni wannan matsayi… Duk da cewa lokacina taƙaitacce ne, amma ina alfahari da ayyukan da na faro”, kamar yadda ya wallafa a shafin nasa.
Haka kuma ya taya sabbin ministocin da aka sanar da naɗinsu, waɗanda ya ce yana da yaƙinin za su ɗora kan ayyukan da suka faro.