fidelitybank

Ina fatan INEC za su dauki darasi a zaben Senegal – Atiku

Date:

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya taya sabon zaɓaɓɓen shugaban Senegal Bassirou Diomaye Faye murnar lashe zaɓen ƙasar da aka yi a ranar 24 ga watan Maris ɗin 2024.

Cikin wani sakon X da ya wallafa a yammacin Juma’a, Atiku ya ce nasarar gudanar da zaɓen lafiya ƙalau, ya nuna akwai kyakkyawan fatan ƙasashen da ke ƙarƙashin mulkin soji su ma za su iya komawa kan tsarin dimokraɗiyya a nan gaba.

“A wajenmu Najeriya da wasu wuraren, akwai babban darasi da ya kamata mu koya a zaɓen Senegal

“Wannan yana ƙara tabbatar da cewa a ƙarƙashin dimokraɗiyya ne ake iya samar da gwamnati mai inganci,” in ji Atiku.

Ya ce abin da aka gani a zaɓukan Najeriya na 2019 da na 2023 sun nuna INEC ba ta yi abin da muka yi tsammani ba.

“Ina taya shugaban Faye murnar lashe zaɓe. Fatana shi ne zaɓen ya zama mai alfanu ga mutanen Senegal kuma ya zama zakaran gwajin dafi ga sauran ƙasashen Yammacin Afrika.”

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp