Tsohon gwamnan jihar Legas, Asiwaju Bola Tinubu, ya ce, damarsa na lashe tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na da yawa.
Tinubu yayi magana ne a ranar Lahadin da ta gabata a ziyarar da ya kai jihar Taraba, domin ganawa da wakilan jam’iyyar APC a jihar.
“Dama na na cin tikitin yana da girma sosai, kuma ina da kwarin gwiwa. Na tabbata zan iya kuma zan ci nasara,” in ji shi.
Da yake magana kan yiyuwar gudanar da tsarin sulhu, Tinubu ya ce, ya fi son tsarin dimokuradiyya kan zaben wanda zai zama dan takarar jam’iyyar APC a zaben shugaban kasa na 2023.